NT4 Sun Saki Sabuwar Waka

Photo source : Instagram account 

By Omar Ayuba Isah

Get Free Music Updates and Mixes on Telegram

Shahararren kungiyar nan ta mawaka Hausa Hip Hop daga kasar Ghana da ke da alaka da Najeriya wadan da aka san su da Nt4 sun saki sabuwar waka mai taken "Wallahi tallahi", a cikin watan nan ta Mayu 2021.

Sun sanar da hakan ne a shafin su na instagram mai mabiya sama da mutun dubu talatin da hudu, inda su ka baiyana cewa tini wannan wakar ta fito a shafukan sauke wakoki daban daban, kuma kamar sauran wakokin su, wannan ma dauke yake da salon Hip Hop mai zafi da maganganu irin na habaici da shagube.

Mutun Dubu Goma Sha Bakwai (17,000) Sun Ga Bidiyon Hamisu Breaker A Ranar Farko.

Nt4 wadan da su ka shahara da fitacciyar wakar su mai taken "Tabanan gana" a duk kasashe da garurruwan Hausa, sun yi wakoki sanannu da dama irin su "Adaidaita", "Conderm" da sauran su. Kuma cikin manyan mawakan da su ka yi waka da su a Najeriya sun hadar da Dj Ab, Adam A zango da dai sauran su.

Tini daukacin masoyan su daga sassa daban daban su ke ta yin bidiyo suna daurawa a shafukan su dan bayan da irin ta su gudunmawar.

Dj Cinch Ya Samu Shedar Kammala Wani Taro Daga Kasar Amurika

Leave your comment