Ina zama dan yin tunani a kan menene so, inji Hamisu Breaker

Photo Credit: Hamisu Breaker (Instagram)

By El-Yaqub Isma'il Ibrahim 

Get Free Music Updates and Mixes on Telegram

Hamisu Breaker yana cikin wata damuwa amma na zuci. Abun da ke cima mawakin tuwo a kwarya shine batun kalmar so da kuma yanin sa. 

Ya bayyana batun dake damun sa ne a kan shafin sa na sada zumunci a kan Instagram. A cewar sa "Sau tarin lokuta, ina zama dan yin tunani akan menene so. Sannan menene dalilin yinsa amma amsar da nafi samu a kansa shine yana wahalar da mai yinsa. sannan yana da dadawa mai yinsa domin shi so, ruwa biyu ne. Allah ka hada da masoyan gaskiya shine fatana a kaina da kuma masoyana #sodanginmutuwa". 

Shahararen Mawaki Sound Sultan Ya Rasu

Hamisu Breaker ya saki sabuwar wakar sa mai taken Sai Dake wanda ta haura har lamba 44 a cikin jerin fitattun wakoki da aka saka a Najeriya a watan Mayu da ta wuce. Sannan wakar ta haura har lamba ta 9 a fitattun wakoki dake tashe a kan shafin kallo na YouTube. 

https://www.youtube.com/watch?v=1eWinSRXuo0

Leave your comment