Mawaki Hazy D-Star zai saki sabuwar waka

Photo Credit - Instagram

By Omar Ayuba Isah

Get Free Music Updates and Mixes on Telegram

Fitaccen mawakin Hausa Hip Hop dan jahar Kano kuma daya daga cikin manyan mawakan jahan Hausa Hip Hop da ke kan gaba a wajan sakin wakoki ma su tashe "Hazy D-Star" da aka fi sani da "Mister Jallabiya" zai saki sabuwar waka bayan lokaci mai tsawo da mawakin ya yi bai fitar da waka ba.

Matashin mawaki Teddy ya saki waka

Wakar mai taken "Ya Kasuwa" wacce fitaccen makadi A-Styl ya yi aikin, shi ne wakar mawaki Hazy D-Star zai fitar a cikin shekarar nan ta 2021, ya sanar da hakan ne a shafin sa na Facebook, inda ya tabbatar da wannan wakar zai fito nan ba da jumawa ba.

Rikicin Mansura Isah da Sani Danja

Tin bayan wakar "Jallabiya" da Hazy ya saki, tauraron mawakin ya kara haskakawa a cikin masana'antar Hausa Hip Hop, daga wannan lokacin, Hazy ya fitar da wakoki daban daban da su ka yi tashe kamar su "Sai Oga", "Go Slow", "Push" da dai sauran su. Tini masoyan Hazy su ka fara banyana ra'ayin su akan wannan sabuwar waka da zai fita, kuma suna ganin ya dace daman ace Hazy ya fitar da waka domin ya kwana biyu bai saki sabuwar waka ba.

Leave your comment