Kundin Waka - Auta Waziri Ya Fitar Da Sabuwar Kundin Wakokin Sa

Photo source : kasheepu instagram account 

By Omar Ayuba Isah

Get Free Music Updates and Mixes on Telegram

Fitaccen matashin mawaki kuma dan asalin jahar Kaduna wanda ke wakar Hausa na salon Nanaye, gargajiya da kuma na siyasa, ya sheda wa masoyan sa fitowar sabuwar kundin wakokin sa wacce ya yiwa suna "Wayasan gobe", sanarwar da Auta Waziri ya yi ta shafin sa na instagram, inda ya tabbatar mu su da cewa, zai fitar da sabuwar waka a ranar sallah karama da za a gudanar a watan Mayu ta shekarar 2021

Daga sunan kundin wakokin, ka na iya nazartar cewa wakokin akan rayuwa da soyayya aka yi su, wanda ya hada da bangaran ta na dadi, daci da kuma rabuwa. Sai dai idan mai karatu ya saurari wakokin ne, sai ya tabbatar da ina wakokin su ka dosa.

Dj Ab Zai Yi Wasan Sallah A Kano

Wannan sabuwar kundin ya kunshi wakoki har guda bakwai (7), wadan da su ka hadar da:

1- Tawa

2- Matan Arewa

3- Wayasan Gobe

4- Matan bana ft Ado Gwanja 

5- Gaskiyar Zance ft Husaini Danko 

6- Ganguna ft Lsvee

7- Zuciya ke kauna

Tini manyan mawaka da kananan su suka daura wannan wakar a shafukan su daban daban dan bada ta su gudunmawar ga mawaki Auta Waziri.

Mawaki Dabo Daprof ya shammaci mutane a garin Danbatta

Leave your comment