Mansura Isah bana ta yi rabon abinci kamar yadda ta saba

Picture source :Mansura I. instagram account

By Omar Ayuba Isah

Get Free Music Updates and Mixes on Telegram

Shahararriyar jaruma Mansura Isah kuma daya daga cikin fitattun matan Arewa ma su taimakawa mara sa karfi ta karkashin gidauniyar su, ta fara rabon abincin bude baki kamar yadda ta saba duk watan Ramadan ta ko wani shekara.

Isah Ayagi ya fitar da sabuwar waka

 

Bana ma dai jarumar ta cigaba da wannan kokari da ta ke wa mara sa karfi, dan su samu abun bude baki bayan sun kai azumi.

Jarumar wacce ta ke samun tallafi daga wasu daidaikun mutane ma su taimakawa da kayan abincin da ita da digauniyar ta su ke girkawa, sun fara ne bana da dafa taliyar wata baiwar Allah da ta ba su gudunmawa dan taimakawa mara sa karfi.

Kamilu koko ya hana ni kudin da Rarara ya bashi ya bani -AleeGee

A rana ta biyu kuma shinkafa da wake su ka dafa tare da mai da yaji, duk da jarumar ba ta nan a lokacin da aka dafa abincin, amma ta yaba wa masu dafa abincin tare da fatan cigaba da hidimtawa Al'umma.

Ahmad Shanawa ya Saki Sabuwar Bidiyo

Leave your comment