An karrama jarumi Ty Shaban a matsayin ma'aikacin gidan TV

Photo source: Ty Shabanfrom  Uniquepikin's Instagram handle)

By Omar Ayuba Isah

Send To A friend On Whatsapp

Babban jarumi kuma ma'aikacin gidan TV na Arewa24 Ty Shaban ya samu karramawa a matsayin ma'aikacin gidan TV a Arewacin Najeriya daya fi kowa hazaka a shekarar 2020.


Wannan karramawar ta fito ne daga bikin karramawa irin sa na farko a jihar zamfara wanda aka hada dan wani bita akan kasuwanci da sana'ar dogaro da kai tare kuma karramawa wasu daga cikin mutanan da su ka nuna bajinta a fanni daban daban a Arewacin Najeriya.


Jarumin wanda ya ke gabata da wani shiri a gidan TV na Arewa24 mai taken "Dandalin Taurari" ya kasance daya daga cikin mutanan da su ke baiwa mawaka da ma jarumai dama ta cikin shirin dan nuna basirar su a fanni daban daban ciki kuwa har da ma wadan da ba waka ko fim su ke ba.

Jarumin ya wallafa wannan karramawa cikin hotunan da ya dauka a ofishin sa da ke cikin garin Kano inda ku ma ya wallafa kotunan a shafin sa na Instagram. Darurruwan masoyan sa ne su ka masa murna tare da Allah sanya alheri da kuma fatan samun cigaba da ya fi wannan.

Leave your comment